Wani Mawaki a Kano ya Maka BBC Hausa a Kotu

Date:

Kotun Tarayya da ke zamanta a Kano ta dage sauraron shari’ar da wani matashin mawaki, Abdul Kamal, ya maka BBC Hausa kan amfani da sautin wakarsa a matsayin taken shirin ‘Daga Bakin Mai Ita’ ba tare da izininsa ba.

A yayin zaman kotun na ranar Litinin, Sashen Hausa na BBC ya nemi kotun ta yi watsi da bukatar mawakin mai suna Abdul Kamal, na biyan s wasu kudi a matsayin diyya daga kamfanin.

Yadda Mota ta Take Wani Mai Kwace Waya da Makami a Kano – Yan sanda

Lauyan BBC, Barista Shakiruddedn Mosobalage, ya bayyana cewa tun da masu kara sun bayyana kudin da suke nema a matsayin tarar amfani da abin da suke kara, to babu bukatar kotu ta bayar da wata oda a kan hakan.

Abdul Kamal ya maka BBC Hausa a gaban kotun ne kan yin amfani da wani sautin kidansa a matsayin taken shahararen shirinsu na ‘Daga Bakin Mai ita’ ba tare da izininsa ba.

Yadda Gobara ta Hallaka Miji da Mata da Yaƴansu 5 a Kano

Lauyansa, Barista Bashir Ibrahim Umar, ya bayyana cewa rokonsu na kan daidai kuma kotu ba ta hurumin yanke wa mutum abin da zai nema a matsayin diyya.

“Idan mai kara ya kai kara dole ne zai fada wa kotu abin da yake so ta yi masa, ba wai ita kotun ce za ta ce ga abin da za a yi wa mai kara ba.”

Alkalin kotun, Mai Shari’a N.M Yunusa, ya dage zaman zuwa ranar 12 ga watan Fabrairu, 2024 don ci gaba da shari’ar.

 

Aminiya

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...