Yanzu-Yanzu: Gwamnan Kano Abba Kabir Ya Sauyawa Ma’aikatar Mata ta Jihar Suna

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf yace gwamnatinsa ta chanza sunan ma’aikatar mata ta jihar zuwa ma’aikatar mata yara da masu bukata ta musamman ta jihar kano.

” Ina so ku sani cewa wannan gwamnatin ta damu da ku, shi yasa tun da muka zo muka chanza sunan wannan ma’aikata kuma mun fara gyaran gidajen masu bukata ta musamman a jihar kano, Inda muka fara da gidan masu tabin kwakwalwa dake tudun maliki”.

Talla

Gwamna Abba Kabir ya bayyana hakan ne yayin taron bada tallafi ga masu bukata ta musamman 2,000 a kano domin su dogara da kawunansu, wanda aka gudanar a gidan gwamnatin jihar.

“Chanza sunan ma’aikatar matar zai taimaka waje sake matso da ku cikin gwamnati, sannan duk abun da za’a yi baza a manta da ku ba, zaku ma cigaba da amfanar wannan gwamnati in Allah ya so”. Inji Abba Kabir

Mataimakin Shugaban Kasa ya Bude Ofishin gwamnan Kano Da Aka Sabunta

Gwamna Abba Kabir yace gwamnatin sa ta bada mukamai daban-daban ga masu bukata ta musamman, kuma yayi alkawarin kara bada wasu mukaman don masu bukata ta musamman su tabbatar gwamnatin bata manta da su ba.

Gwamnan dai ya yi alkawarin cigaba da bujiro da aiyuka da tallafin da zai shafi masu bukata ta musamman kai tsaye da su da kuma ‘ya’yan su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...