Mataimakin Shugaban Kasa ya Bude Ofishin gwamnan Kano Da Aka Sabunta

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Mataimakin Shugaban Nigeria Kashim Shattima ya jagoranci bude ofishin Gwamnan Kano da aka sabunta dake gidan gwamnatin jihar.

Da yake bude ofishin, wanda gwamnatin jihar Kano ta sabunta, mataimakin shugaban kasa Kashim Shattima ya jinjinawa Gwamnan Kano bisa ayyukan raya kasa da yake aiwatar wa al’ummar a jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labarai na gwamnan Kano sanusi Bature Dawakin tofa ya aikowa kadaura24.

Talla

Rahotanni sun bayyana cewa Kashim Shatima ya zo jihar Kano ne, domin halartar jana’izar tsohon shugaban majalisar wakilan Nigeria marigayi Ghali Umar Na’abba, wanda aka yi jana’izarsa da yammacin Jiya Laraba.

Hotunan yadda akai Jana’izar Tsohon Kakakin Majalisar Wakilai Ghali Na’Abba

Haka kuma Kashim Shatima ya miƙa saƙon ta’aziyya ga gwamnatin Kano da iyalan mamacin a madadin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tunubu, inda ya bayyana mutuwar a matsayin babban rashi wanda baza’a iya mantawa da shi ba, bisa mahimmancinsa ga al’umma.

A yayin bude ofishin gwamnan, da kuma zuwa ta’aziyyar mataimakin shugaban ƙasar ya sami rakiyar mataimakin shugaban majalisar Dattijai Barau Jibrin, da sanatan Kano ta Kudu Abdurrahman Kawu Sumaila, da wasu ƴan majalisar tarayyar Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...