Da dumi-dumi: Tinubu Ya Nada Mai Taimakawa Kan Al’amuran Nakasassu

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Shugaban ƙasar Nigeria Bola Tinubu ya amince da nadin Muhammad Abba Isa a matsayin babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin masu bukata ta musamman.

A cewar wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya fitar a ranar Alhamis, yace nadin na cikin kudirin Tinubu na tabbatar da cewa kowane bangare na al’umma ya samu isasshiyar dama a gwamnatin sa.

Talla

”Muhammad Abba Isa fitacce ne wanda ya kwashe sama da shekaru 10 yana bada shawarwarin yadda za’a inganta rayuwar Masu bukaci ta musamman a gida Nigeria da kasashen waje,” in ji sanarwar.

Yan kwadago sun rufe titin zuwa filin jirgin sama na Abuja

‘’Sabon mai taimaka wa shugaban kasa ya kammala karatunsa kan harkokin mulki a jami’ar Maiduguri, inda kuma yayi Digirin na biyu a wannan fannin a dai jami’ar ta Maiduguri a shekarar 2017.

Shugaban ya bukaci sabon mai bashi shawara da ya samar da hanyoyin da za a bi don shigar da masu bukata ta musamman cikin manufofi da shirye-shiryen dukkan ma’aikatu, sassan da hukumomin gwamnatin tarayya tare da yin aiki kafada da kafada da kananan hukumomi don aiwatar da shirin, don inganta rayuwar su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...

Ba a ga watan Zulqida a Nigeria ba – Sarkin Musulmi

Daga Unmahani Abdullahi Adakawa   Mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad...

Hukumar Shari’a ta Kano ta Gargadi Alkalai 2, ta kuma dakatar da Magatakarda 2

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Hukumar kula da shari’a ta jihar...

Amarya Aisha Humaira ta aike da sako ga masu kage kan alakarsu da Rarara

  Aisha Humaira, amaryar kuma abokiyar aikin mawaki Dauda Kahutu...