Yanzu-Yanzu: Tinubu Yayi Sabbin Nade-nade a ofishin mataimakin Shugaban kasa

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Shugaban kasar Nigeria Bola Tinubu ya nada Kingsley Stanley Nkwocha, tsohon Manaja kuma Editan Jaridar Leadership, a matsayin Babban Mataimaki na Musamman (SSA) kan Harkokin Yada Labarai da Sadarwa a Fadar Shugaban Kasa.

 

Kadaura24 ta rawaito An nada Nkwocha ne tare da wasu da dama da za su yi aiki a ofishin mataimakin shugaban kasa.

Talla

Tinubu ya kuma nada Tope Fasua, babban jami’in gudanarwa na Global Analytics Consulting, a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin tattalin arziki a ofishin mataimakin Shugaban kasa .

Da dumi-dumi: Kotu ta yanke hukunci kan zaɓen gwamnan jihar Zamfara

A cikin jerin sunayen, wasu da aka nada a ofishin mataimakin shugaban kasar sun hada da Sadiq S Jambo a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin tattalin arziki, Dr. Muhammad Bulama, a matsayin babban mataimaki na musamman kan aiyuka na musamman, Mahmud Muhammad a matsayin mataimaki na musamman na cikin gida, da Ahmed Ningi a matsayin babban mataimaki na musamman kan kafafen yada labarai na zamani da bada agajin gaggawa.

Sauran su ne Stanley Nkwocha mataimakin na musamman kan harkokin yada labarai a ofishin mataimakin Shugaban kasa, sai Tope Kolade Fasua, Mashawarci na Musamman Tattalin Arziki da Sadiq S Jambo Mai baiwa mataimakin Shugaban kasa Shawara kan harkokin tattalin arziki.

Gimba Kakanda, marubuci kuma manazarci kan harkokin jama’a, Tinubu ya nada shi a matsayin Babban Mataimaki na Musamman, kan harkokin Bincike da fashin baki a ofishin mataimakin Shugaban kasa.

Sai Dr. Hakeem Baba Ahmad a matsayin Mai baiwa mataimakin Shugaban kasa Shawara kan harkokin siyasa da Kuma Dr. Aliyu Moddibo mai baiwa mataimakin Shugaban kasa Shawara kan dukkanin al’amura.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...