Da dumi-dumi: Kotu ta yanke hukunci kan zaɓen gwamnan jihar Zamfara

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Zamfara ta kori karar da jam’iyyar APC ta shigar, ta kuma tabbatar da nasarar Dauda Lawan, a matsayin halastaccen zababban Gwamnan jihar Zamfara.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito bayan da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana Dauda Lawan na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar, hakan tasa Bello Muhammad Matawalle na jam’iyyar APC ya shigar da kara Inda yake ƙalubalantar nasarar da Dauda Lawan ya samu a gaban kotu.

Talla

 

A zaman yanke hukunci da kotun ta yi yau a birnin Sokoto, ta ce Dauda shi ne ya samu ƙuri’u mafi yawa a zaɓen.

 

Tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle ne ya shigar da ƙara yana ƙalubalantar nasarar Dauda a kotun wadda ke zaman ta a birnin Sokoto.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...