Yanzu-Yanzu: Tinubu ya sake nada sabbin ministoci guda 2

Date:

 

Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da nadin Dr. Jamila Bio Ibrahim a matsayin ministar matasa, har zuwa lokacin da majalisar dattawan tarayyar Najeriya ta amince da ita.

 

Shugaban ya kara amincewa da nadin Mista Ayodele Olawande a matsayin karamin ministan matasa, har zuwa lokacin da majalisar dattawan tarayyar Najeriya ta amince da shi.

Talla

Kadaura24 ta rawaito Hakan dain na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Shugaban kasa Ajuri Ngelale ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

Zamu samar da ingantacceen tsarin samar da gidaje ga yan Nigeria – ATM Gwarzo

Dokta Jamila Bio Ibrahim matashiyar likita ce kuma a baya-bayan nan ta taba rike mukamin shugabar kungiyar Matasa ta (PYWF). Ta kuma yi aiki a matsayin babbar mataimakiya ta musamman ga gwamnan jihar Kwara kan maradun ci gaba mai dorewa (SDGs).

Shi kuwa Mista Ayodele Olawande kwararre ne wajen sha’anin ciyar da al’umma kuma shugaban matasa a jam’iyyar APC mai mulki. Kwanan nan ya yi aiki a ofishin mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan kirkire-kirkire daga 2019 zuwa 2023.

Shugaba Tinubu ya bukaci wadanda aka nadan da su tabbatar da cewa suna nuna kwazo da kuma kawo cigaba ga matasan Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...