Barazanar kisa: NBA ta yabawa Gwamnan Kano, ta bukaci jami’an tsaro su fara bincike

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Kungiyar lauyoyi ta Najeriya (NBA) ta yabawa gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf kan matakin gaggawa da ya dauka na korar wasu mukarrabansa guda biyu sakamakon barazanar kisan alkalan kotunan sauraren kararrakin zaben da kuma kalaman batanci ga mataimakin shugaban kasa.

Kadaura24 ta rawaito, Idan dai za a iya tunawa, kwamishinan kasa da safayo, Adamu Aliyu Kibiya a ranar Alhamis a wani taron addu’a na musamman da magoya bayan jam’iyyar NNPP suka gudanar, inda ya yi barazana ga alkalan kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da cewa duk wanda a cikinsu ya karbi cin hanci don murde hukuncin sai dai ya zabi ko kuɗi ko rayuwarsa.

Talla

Har ila yau, mai ba gwamna shawara na musamman kan harkokin matasa da wasanni, Yusuf Imam, wanda aka fi sani da Ogan Boye, a wani faifan bidiyo a ranar Alhamis yayin taron addu’o’i na musamman da NNPP ta gudanar yayi kalaman batanci ga mataimakin shugaban kasa, Khasim Shettima da kuma tunzura al’umma.

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya Baiwa Kwamishinonisa Sabon Umarni

Da yake zantawa da SOLACEBASE kan ci gaban, Shugaban kungiyar lauyoyin na Kano, Barr. Suleiman Gezawa ya yaba wa gwamnan jihar kan matakin korar mukararabanwa kan kalaman da sukai da kuma nisanta gwamnatinsa da kalaman da sukai .

Daga nan Gezawa ya yi kira ga jami’an tsaro da su kaddamar da bincike kan barazanar kisa da kwamishinan ya yi wata kila akwai wata makarkashiya a cikin wannan barazanar ta shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...