Yada hotunan Zara Beyero Haramun ne – Hukumar Hisbah

Date:

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano da ke ta yi kira ga masu yada hotunan ‘yar Sarkin Bichi, Zarah Nasiru Ado Bayero wadda Dan shugaban kasa Yusuf Buhari zai aura, da su guji yin hakan “saboda ya saba wa Shari’ar Musulunci”.

Kwamandan Hisbah Harun Muhammad Ibn-Sina ya ce aikin hukumar shi ne hana yada barna ko da kuwa ta faru a baya, ba wai “tonowa da kuma hukunta mutum ba”.

Kiran na Hisbah ya biyo bayan dubban ra’ayoyi da mutane suka dinga bayyanawa a shafukan zumunta cikin kwana uku da suka wuce bayan hotunan amarya Zarah sun karaɗe shafukan sanye da wata doguwar riga.

A cikin hotunan wadanda ba a gan ta tare da angon ba, babu dan kwali a kan gimbiyar ta Masarautar Bichi da ke Kano sannan kuma saman rigar yana da launin fatar jikinta.

Wasu bayanai sun ce hotunan sun ɓulla ne daga wani bikin mata zalla da aka gudanar a Abuja a wannan makon.

Wannan ne ya sa masu amfani da shafukan zumunta suka dinga kira ga Hisbah da ta ɗauki mataki, inda sunan hukumar ya kasance daya daga cikin manyan batutuwan da aka fi tattaunawa a kafofin na Najeriya tun daga ranar Laraba zuwa Juma’a.

Hukumar Hisbah ta Kano wadda aka sani da tabbatar da bin dokokin Musulunci, ta ce yada hotunan “ya saɓa wa Shari’ar Musulunci”.

Cikin wata hira da manema labarai, Kwamandan Hisbah Harun Muhammad Ibn-Sina ya ce ba aikin hukumar ba ne tonowa tare da kama masu laifi, aikinsu shi ne hana yaɗa ɓarna.

77 COMMENTS

  1. Allah sarki talaka babu inda doka take aiki sai akan talaka dan Yanzu da talaka ne yayi wannan aikin Da tuni an kama a halinsa amma saboda masu kwali a idone babu abunda zai fara
    Kukan kuciya jawabe ne

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...