Marayu 100 a kano sun rabauta da Tallafin Naman Sallah daga Falakin Shinkafi

Date:

 

Kimanin Marayu 100 sun Amfana da tallafin Naman Sallah da Barka da Sallah a unguwar Yakasai Daga Wani Dan Kasuwa Kuma Dan kishin Kasa Ambasada Yunusa Yusuf Hamza ( Falakin Shinkafi).

Da yake Zantawa da Wakilin Kadaura24 Jim kadan bayan kammala rabon Falakin Shinkafin Amb. Yunusa Yusuf yace ya tallafawa marayun ne domin Sanya farin Ciki a zukatansu a Wannan Lokaci na Sallah Babba.

Yace Marayu Suma’ya’yane da ya kamata a Rika kula dasu Musamman a Lokaci irin Wannan domin a dauke musu radadin Rashin Iyayen su.

Amb. Yunusa Yusuf yace ya Zama wajibi mawadata su Rika tallafawa marayu don kyautata Rayuwar su, “Idan ba’a taimaki Rayuwar su ba hakan ce take sawa su taso basa tausayi Kuma su zamo gurbatattu Saboda da Suma ba’a taimaki Rayuwar suba.

” Ina Amfani da Wannan dama wajen Kira ga Shugabanni da mawadata dasu Rika tallafawa marayu don inganta Rayuwar tare da Samun lada Mai yawa a wajen Allah”. Inji Falakin Shinkafin

Wasu Daga Cikin Iyayen Marayun da Suka Amfana da tallafin sun yabawa Ambassador Yunusa Yusuf Hamza (Falakin Shinkafin) bisa tallafin da ya Baiwa ya’yansu, Inda Suka ce dama ya saba gudanar da irin Wannan tallafi ta karkashin Kungiyar Yakasai Zumunta.

Kadaura24 ta rawaito bayan Naman Sallah Marayun sun rabauta da kudi da Kayan more Rayuwa don faranta musu a Wannan Lokaci na Sallah.

98 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Daura ya nuna inda za’a binne shi idan ya rasu.

  Mai Martaba Sarkin Daura dake jihar katsina Alhaji Dr....

Na sauke nauyin da Tinubu ya ɗora min – Gwamnan riko na jihar Rivers

Vice-Admiral Ibok-Ete Ibas (Mai ritaya), wanda shi ne gwamnan...

Cin Gashin Kan Kananan Hukumomi: Kawu Sumaila ya jinjinawa Gwamnan Kano

Sanatan da ke wakiltar Kano ta Kudu a Majalisar...

Gwamna Yusuf Ya Shirya Baiwa Kananan Hukumomin Kano Cikakken ‘Yan cin Kai

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...