KAYYASA! : Awanni kadan kafin saukarsa, Ganduje ya Rantsar da Sabon kwamishina

Date:

Daga Kabiru Yusuf

Awanni kadan kafin ya sauka gwamnan jihar Kano mai barin gado Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya rantsar da sabon kwamishina a hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar kano KANSEC.

 

Kwamishinan shari’a na jihar Kano Barr. M A Lawan ne ya rantsar da sabon kwamishinan mai suna Abdullah Abba Sumaila, yayin taron majalisar zartarwar jiha na ƙarshe wanda ya gudana daren jiya a gidan gwamnatin kano.

 

Da yake jawabi bayan rantsar da sabon kwamishinan gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya ce an rantsar da kwamishinan ne bayan majalisar dokokin jihar kano ta tantance tare da Amincewa da nada shi a matsayin kwamishina.

 

” Muna fata zaka yi aikin ka yadda ya dace saboda muhimmancin da hukumar zabe take da shi musamman wajen shirya zaben kananan hukumomi a jihar kano”.

 

An dai rantsar da sabon kwamishinan ne awanni kasa da 48 a rantsar da sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar kano Engr. Abba Kabir Yusuf.

 

Sai dai mukamin kwamishina irin wannan na wannan hukumar ba kamar sauran kwamishinoni na siyasa da aka Sani ba , domin shi wa’adi ne da shi na kamar yadda doka ta gindaya .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Likitocin Jinya da Ungozoma sun janye yajin aiki – Ministan lafiya

Ƙungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Ƙasa (NANNM) ta...

Sarkin Hausawan Arewa, Amb. Balarabe Tatari, Ya Aike da Sakon Ta’aziyyar Buhari da Dantata

Sarkin Hausawan Arewa kuma Ambasadan Zaman Lafiya, Alhaji Balarabe...

INEC ta sanya ranar fara rijistar masu zabe a Nigeria

Hukumar zaɓen Najeriya ta ce nan gaba cikin wannan...