Laylatul Qadir : Fiye da mutune miliyan biyu ne suka halarci sallar dare a masallatan Harami

Date:

Daga Safiyanu Dantala Jobawa

 

Fiye da masallata miliyan biyu ne suka halarci masallacin harami da ke Makka da kuma masallacin Annabi da ke Madina domin halartar sallolin tarawi a daren ranar 27 ga watan Ramadan don neman dacewa da daren Laylatul Qadari.

 

Jaridar Saudi gazzet ta ruwaito shugaban masallatan biyu masu alfarma Sheikh Abdul Rahman Al-Sudais ne ya bayyana haka a lokacin da yake yaba wa tsare-tsaren da masalallatan suka yi domin bai wa masallata damar gudanar da ibadunsu cikin kwanciyar hanakali

Da dumi-dumi : INEC ta bayyana Matsayarta kan Zaben Gwamnan Jihar Adamawa

Ya ce kusan masu ibada miliyan ɗaya da rabi ne suka halarci sallar dare a masallacin harami da ke Makka, wanda Sheikh Abdul Rahman Al-Sudais ɗin ya jagoranta.

 

Akan samu tururuwar masu sallar dare a dararen ranakun mara musamman dare 27 domin neman dacewa da daren Laylatul Qadr, saboda tarin alkairan da ke tattare da daren.

 

Hukumomin Saudiyya sun samar da wadatattun jami’an tsaro waɗanda suka taimaka wa masu ibada wajen gudanar da ibadunsu cikin tsari, da kwanciyar hankali duk kuwa da irin cunkoson jama’a da aka samu a wajen ibadar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...