Da dumi-dumi:INEC ta bayyana Alhassan Doguwa a matsayin wanda ya lashe zaben Doguwa da Tudun Wada

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Hukumar Zaɓe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai ta kasa Alhasan Ado Doguwa a matsayin wanda ya lashe zaben dan majalisar tarayya da zai sake wakiltar kananan hukumomin Doguwa da Tudun wada.

 

Jami’in zaben, Farfesa Sani Ibrahim, wanda ya bayyana sakamakon zaben a zaben da aka kammala na mazabu takwas a karamar hukumar Tudunwada, ya ce Doguwa ya samu kuri’u 41,573.

 

Babban abokin hamayyarsa, Yushau Salisu na jam’iyyar NNPP ya samu kuri’u 34,831, kamar yadda jaridar r Daily Trust ta rawaito.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a zaɓen da aka gudanar a Ranar 25 ga watan fabarairun shekara 2023, an bayyana Alhassan Ado a matsayin wanda ya lashe zaben, sai dai daga bisani hukumar zabe ta ce takurawa Baturen zaɓen aka yi ya bayyana sakamakon, bayan kuma zaɓen bai kammala ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...

Zargin kwace gona: Majalisar Dokokin Kano zata binciki Shugabar Karamar Hukumar Tudun Wada (ALGON)

    Majalisar dokokin jihar Kano, ta sha alwashin gudanar da...

Tinubu ya yi wa Buhari abun da Buharin ya kasa yi wa kakana- Jikan Shagari

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Nura Muhammad Mahe, jikan tsohon shugaban...