Dalibai matan da aka sace na Jami’ar Tarayya ta Gusau sun shagi Iskar  ‘yanci

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

A ranar Juma’ar nan ne daliban nan mata guda biyu na jami’ar tarayya ta Gusau da aka sace a masaukinsu na haya dake kauyen Sabon Gida da ke karamar hukumar Bungudu sun samu ‘yanci a yau Juma’a.

 

Kungiyar dalibai ta jihar Zamfara (ZAMSSA) reshen jami’ar tarayya ta Gusau ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta rabawa manema labarai mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na kungiyar, Kwamared Umar Abubakar .

 

Ko da yake ba a bayyana ko an biya kudin fansa ko ba’a biya ba kafin a sako daliban Sashen Microbiology na jami’ar.

 

“Daliban mata biyun da aka sace na Sashen Microbiology na jami’ar sun koma cikin yan uwansu da sanyin safiyar ranar Juma’a 14 ga Afrilu, 2023 cikin koshin lafiya bayan kwanaki 12 a hannun yan ta’addan.” a cewar sanarwar

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...

Zargin kwace gona: Majalisar Dokokin Kano zata binciki Shugabar Karamar Hukumar Tudun Wada (ALGON)

    Majalisar dokokin jihar Kano, ta sha alwashin gudanar da...