Mutane biyar sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Bauchi

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

Hukumar kiyaye haɗura reshen jihar Bauchi ta tabbatar da mutuwar mutum biyar da suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota a kan babbar hanyar Bauchi zuwa Jos kusa da ƙauyen Panshanu.

Hukumar ta ce hatsarin ya faru ne da sanyin safiyar jiya Laraba bayan da wata mota ƙirar Toyota ta gamu da ta Peugeot waɗanda duka ke ɗauke da fasinjoji a cikinsu bayan da motar ta kuɓcewa ɗaya daga cikin direbobin.

DSS ta ce ta gano makarkashiyar kafa gwamnatin rikon kwarya a Nigeria

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa maza biyar da ke cikin motar duk sun mutu bayan da suka ƙone kurmus saboda kama da wuta da motocin suka yi.

An mika gawarwakin mutanen tare kuma da motcin zuwa hannun hukumar ƴan sanda shiyyar Toro da ke jihar ta Bauchi.

Yanzu-Yanzu: Nasiru Gawuna ya taya Abba Gida-gida Murnar lashe zaɓen gwamnan Kano

Haka-nan ma a jihar Kebbi, mutum 35 ne suka rasa rayukansu a ranar Laraba a wasu haɗura biyu da suka afku tsakanin 26-27 ga watan Maris, a cewar hukumar kiyaye haɗura a jihar.

Babban kwamandan hukumar a jihar, Yusuf Haruna Aliyu, ya ce an samu nasarar ceto mutum 40 daga haɗarin. Ya ce hatsarin ya faru ne tsakanin wasu motoci guda uku waɗanda ke ɗauke da mutum 75 a cikinsu.

Ya ce an garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibiti a Jega da kuma Kalgo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Neman Ilimin addini dana boko da sana’a ba kishiyoyin juna ba ne – Dr. Aminu Sagagi ga matasan Zango

Daga Rahama Umar Kwaru   Wani Malamin addinin musulunci a kano...

Kotu Ta Ɗage Sauraron Ƙarar DA ICPC ta Kai Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta Ta Jihar Kano

    Babbar kotun tarayya mai lamba shida(6) dake Babban Birnin...

Kisan ɗalibai a Kano: Kwamitin Malamai da Iyayen yara na jihar ya nuna damuwarsa

Daga Abdulhamid Isah D/Z Malam Salisu Abdullahi shugaban kwamitin malamai...