Daga Aliyu Abdullahi Fagge
Gwamna Nyesom Wike na jihar Rivers a ranar Juma’ar da ta gabata ya yi ikirarin cewa fadar shugaban kasa tana goyon bayan Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben dake tafe nan da makwanni uku masu zuwa.
Wike ya bayyana hakan ne a garin Ibaka da ke tsibirin Okrika yayin gangamin yakin neman zaben jam’iyyar PDP na karamar hukumar Okrika a jihar Rivere.

Ya kuma ƙalubalanci sauyin kudin naira da aka yi, Inda yace a matsayin su na yan adawa suna bukatar shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sake duba batun aiwatar da manufofin.

Ya kara da cewa Atiku da magoya bayansa a kwanakin baya sun bayyana cewa ba sa bukatar Gwamnonin G-5 kafin su ci zabe, Saboda goyon bayan wasu mutane da suke samu daga fadar shugaban kasa.
A cewarsa, “Su (Atiku da magoya bayansa) suna ganin an ba su tabbacin zasu ci zabe, amma Ina so su sani zaben bana mutane ne zasu yanke hukunci ba wai wasu mutane a fadar shugaban kasa ba.
Dangane da batun sabon tsarin kudin, gwamnan Rivers ya ce, “Wannan manufar ta musgunawa mutane ce, inda yace mutane da kudaden su a bankuna amma an hana su.