Zaben 2023: Fadar Shugaban Kasa na Goyon Bayan Atiku – Wike

Date:

Daga Aliyu Abdullahi Fagge

 

Gwamna Nyesom Wike na jihar Rivers a ranar Juma’ar da ta gabata ya yi ikirarin cewa fadar shugaban kasa tana goyon bayan Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben dake tafe nan da makwanni uku masu zuwa.

 

Wike ya bayyana hakan ne a garin Ibaka da ke tsibirin Okrika yayin gangamin yakin neman zaben jam’iyyar PDP na karamar hukumar Okrika a jihar Rivere.

Talla

Ya kuma ƙalubalanci sauyin kudin naira da aka yi, Inda yace a matsayin su na yan adawa suna bukatar shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sake duba batun aiwatar da manufofin.

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

 

Ya kara da cewa Atiku da magoya bayansa a kwanakin baya sun bayyana cewa ba sa bukatar Gwamnonin G-5 kafin su ci zabe, Saboda goyon bayan wasu mutane da suke samu daga fadar shugaban kasa.

 

 

A cewarsa, “Su (Atiku da magoya bayansa) suna ganin an ba su tabbacin zasu ci zabe, amma Ina so su sani zaben bana mutane ne zasu yanke hukunci ba wai wasu mutane a fadar shugaban kasa ba.

 

 

Dangane da batun sabon tsarin kudin, gwamnan Rivers ya ce, “Wannan manufar ta musgunawa mutane ce, inda yace mutane da kudaden su a bankuna amma an hana su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...