Siyasar Zamfara:Mu nai maka maraba da zuwa APC,Amma da Sharudda – Abdulaziz Yari

Date:

Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara a ranar Litinin sun yi wani taro a jihar Kaduna inda suka tattauna kan sauya shekar da gwamnan jihar, Bello Matawalle ya yi zuwa jam’iyyar.


 Taron ya samu halartar tsoffin gwamnonin jihar Zamfara biyu, Abdulaziz Yari da Mahmud Shinkafi, da tsoffin sanatoci, ministoci da shugaban APC na jihar, Lawal M Liman.


 Da yake zantawa da manema labarai bayan taron, tsohon Gwamnan, Abdulaziz Yari, wanda kuma shi ne jagoran APC a Zamfara, ya ce bayan tattaunawar da sukai, sun yanke shawarar tarbar Gwamna Bello Matawalle cikin jam’iyyar duk da turjewar da suka yi da farko, da sharadin zai ci gaba  bin ka’idojin jam’iyyar da akidunta na Samar da ci gaba.

 Ya ce duk da cewa Gwamna Matawalle ya gaza gudanar da shugabanci na Gari da hada kan daukacin mutanen jihar tun hawan sa mulki, APC a matsayin uwa Daya uba daya za ta ba shi damar zama a cikin jam’iyyar tare da fatan zai mutunta ka’idoji da Dokokin  jam’iyyar don cigaban al’ummar jihar Zamfara.


 A halin da ake ciki, Kwamitin Aiki na Jam’iyyar PDP ya rushe Kwamitin zartarwar ta a jihar Zamfara, tare da gargadin cewa gwamnan zai rasa kujerarsa bayan sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.


 Sakataren yada labaran na kasa, Kola Ologbondiyan, a wani taron manema labarai a ranar Litinin din nan ya bayyana hakan, ya kuma ce jam’iyyar za ta garzaya kotu don kalubalantar ficewar gwamnan daga jam’iyyar.

97 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...