Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar hutun Maulidi a Nigeria

Date:

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Talata, 25 ga Agusta, 2026, a matsayin ranar hutu ta kasa domin bikin ranar Maulidi, wato zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad (SAW).

Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya sanar da hakan a madadin gwamnatin tarayya, cikin wata sanarwa da babbar sakatariyar ma’aikatar, Dr Magdalene Ajani, ta fitar a ranar Juma’a.

IMG 20260504 WA0036(1)
Talla

Tunji-Ojo ya taya Musulmi a Najeriya da mazauna kasashen waje murnar wannan rana, tare da kira ga ‘yan kasa da su yi tunani kan darussan tausayi, tawali’u da hidima ga al’umma da ke cikin rayuwar Annabi Muhammad (SAW).

Ministan ya ce bikin Maulidi wata dama ce ga al’umma ta yin tunani kan wadannan dabi’u da kuma yadda za a amfani da su wajen gina kasa mai zaman lafiya da hadin kai.

Ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su yi amfani da wannan lokaci wajen yin addu’ar samun zaman lafiya da hadin kan kasa, yana mai jaddada cewa kare hadin kan Najeriya nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa.

IMG 20260728 WA0005
Talla

Tunji-Ojo ya bukaci jama’a da su gudanar da bukukuwan cikin natsuwa da mutunta juna, tare da yi wa al’ummar Musulmi fatan yin Maulidi mai cike da farin ciki da zaman lafiya.

Ya kara tabbatar da aniyar gwamnatin tarayya na ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma tare da tabbatar da dorewar zaman lafiya a fadin kasar.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

‎Hukumar Ilimin Manya ta Kano ta shirya taron horas da manyan ma’aikatanta don inganta aikinsu

‎ ‎Hukumar Ilimin Manyan Makarantu ta Jihar Kano ta bukaci...

‎Tsofaffin Kansilolin Kano Sun Zama Manyan Jakadun Gwamnan Abba Gida-Gida na Asali – Waiya

‎ ‎Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar...

‎Ana ci gaba da kiraye-kirayen a saki Maryam Shehu da EFCC ta tsare sama da kwanaki 30

‎ ‎Daga: Sani Magaji Garko ‎ ‎Ana ci gaba da samun kiraye-kirayen...

‎Tinubu Ya Ƙara Ƙaimi Wajen Ƙarfafa Tsaro a Arewacin Najeriya – Alfindiki

‎ ‎Jigo a jam'iyyar APC a jihar Kano Hon. Faizu...