Tsohon shugaban kungiyar yan jaridu Abbas Ibrahim ya zama dan takarar mataimakin gwamna na jam’iyyar LP a Kano

Date:

Tsohon shugaban kungiyar ’yan Jarida ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Kano, Comrade Abbas Ibrahim, ya zama dan takarar mataimakin gwamna na Jam’iyyar Labour Party (LP) a Jihar Kano, gabanin babban zaben 2027.

IMG 20260704 WA0007
Talla

Abbas Ibrahim ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce ya yanke shawarar yin murabus daga mukaminsa na Wakilin Amintattu na Kasa (National Trustee) na NUJ, Zone A, domin samun damar mayar da hankali kan sabon nauyin da aka dora masa.

IMG 20260728 WA0005
Talla

Ya ce, “Cikin kaskantar da kai, godiya da kuma kishin abokan gwagwarmaya, ina sanar da ku cewa bayan na zama dan takarar mataimakin gwamna na Labour Party da aka sake tsara ta a Jihar Kano, na yanke shawarar yin murabus daga matsayina na National Trustee na NUJ, Zone A.”

Ya kara da cewa murabus din zai ba shi damar sadaukar da isasshen lokaci da kuzari wajen gudanar da wannan sabon nauyi tare da taka rawa sosai a harkokin siyasa.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin ya buƙaci musulmi su fara dubban watan Maulidi

Fadar Sarkin Musulmi ta Sokoto ta yi kira ga...

Auren Zawarawa Da Gwamnatin Kano Ta Yi Haramun Ne — Sheik Hadi MaiHula

Daya daga cikin fitattun Malaman Addinin Musulunci a nan...

Kotu Ta Tura Mutane Biyu Gidan Yari Kan Zargin Rushe Gadar Watari Da Yanka Filaye Ba Bisa Ka’ida Ba

 Kotun Majistare mai lamba 47 da ke Unguwar Zangero...

Kwamishina Waiya Ya Gargadi Kan Yada Jita-jita Game da Shirin Auren Gata a Kano

Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar...