A karni sau daya Allah ya ke yin mutum irin Sarkin Kano Sanusi II – Falakin Shinkafi

Date:

Falakin Shinkafi, Amb. Yunusa Yusuf Hamza, ya ce alfarma ce babba mutum irin Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya kasance a cikinta.

Falakin Shinkafi ya bayyana hakan ne cikin sako taya sarki Sanusi II murnar cika shekaru 65 da haihuwa.

IMG 20260704 WA0007
Talla

Ya ce Sarki Sanusi II mutum ne da yake da jajircewa wajen cimma burikansa, hakan tasa ya sami nasarori masu yawa a rayuwarsu.

“Da ya dauki harkar ilimin addini sai da ya kai makura, haka da ya fara ilimin boko sai sa ya zama Dr. Haka a harkarsa ta banki sa da ya zama gwamnan Babban Bankin Nigeria (CBN), don haka na ce shi na daban ne a cikin al’umma “. Inji Falakin Shinkafa

IMG 20260728 WA0005
Talla

Falakin Shinkafi ya ce a sanadiyyar jajircewar Sarkin Kano Sanusi II jihar Kano da Nigeria sun sami cigaba musamman ta fuskar tattalin arzikin ta hanyar masu zuba jari.

Amb. Yunusa Yusuf Hamza ya ce a madadin ji kansa da iyalansa yana taya sarkin murnar cika wadannan shekaru masu tarin albarka.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar ‘Yan Sandan Kano Ta Cafke Mutane 10, Ta Ceto Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kano ta samu nasarar ceto...

‎Gwamnan Kano Abba Ya Taya Sarki Muhammadu Sanusi II Murnar Cika Shekaru 65

‎ ‎ ‎Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya taya...

‎Muhuyi Ya Gargaɗi ’Yan Siyasa Kan Neman Sakin ’Yan Daba Da Masu harkar Miyagun Ƙwayoyi a Kano

‎ ‎Shugaban Kwamitin Haɗin Gwiwa na Jihar Kano kan Yaƙi...

Gobarar Kasuwar Singer: Tawagar Kano Ta Matsa Lamba ga Tinubu Domin Sakin Tallafin Naira Biliyan 5 ‎

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa‎Wata babbar tawaga da ta ƙunshi...