Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya umarci Hukumar Yaki da Masu Yi wa Tattalin Arziki Ta’annati ta EFCC da Hukumar ICPC mai yaki da cin hanci da rashawa da su sanya ido kan yadda za a raba takin zamani na tallafi a fadin jihar domin tabbatar da gaskiya, adalci da rikon amana.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya aikowa Kadaura24 .
Gwamna Abba ya bayar da wannan umarni ne yayin kaddamar da rabon manyan motoci 150 dake dauke da takin zamani na tallafi ga manoma a kananan hukumomi 44 na jihar.

Ya bayyana cewa an shigar da EFCC da ICPC cikin aikin ne da nufin tabbatar da cewa takin ya isa hannun manoma na gaskiya, tare da dakile karkatar da shi, boyewa ko wasu hanyoyin amfani da shi ba bisa ka’ida ba.
Gwamnan ya kuma bukaci shugabannin kananan hukumomi 44 da su gudanar da rabon cikin gaskiya, adalci da rikon amana, yana mai cewa shirin zai taimaka wajen rage kudin noma, kara yawan amfanin gona da kuma inganta samar da wadataccen abinci a jihar.

Ya yi gargadin cewa duk wanda aka samu da hannu wajen karkatar da takin ko kawo cikas ga shirin zai fuskanci hukunci bisa tanadin doka.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na tabbatar da gaskiya, rikon amana da kuma amfani da dukiyar al’umma yadda ya kamata, yana mai bayyana noma a matsayin ginshikin tattalin arzikin Jihar Kano.