‘Yan sandan Kano za su fara kama masu rufe lambobin mota

Date:

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta sanar da fara aiwatar da dokar hana amfani da motocin da ake rufe lambobinsu, da kuma wadanda ba su da lambar.

A wata sanarwa da kakakin rundunar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar, ya ce matakin ya fara aiki nan take a fadin jihar Kano.

IMG 20260504 WA0036(1)
Talla

Rundunar ta ce rufe ko cire lambobin mota na hana jami’an tsaro gano motocin da ake amfani da su wajen aikata laifuka kamar fashi da makami, garkuwa da mutane, da safarar miyagun kwayoyi.

Gwamnatin Kano ta yi wa Kwankwaso bankada kan kudin fansho

Sanarwar ta ce za a kwace motocin da suka karya dokar tare da gurfanar da direbobinsu a gaban kotu, ba tare da sassauci ba.

‘Yan sanda sun kuma bukaci masu ababen hawa su tabbatar da cewa motocinsu suna da ingantattun lambobin masu rajista a gaba da baya, tare da cire duk wani abin da ke hana ganin lambobin a fili.

IMG 20251224 WA0004

Rundunar ta jaddada cewa ba a ɗauki matakin don a takura wa wasu ba, sai dai don inganta tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Kano.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi wa Kwankwaso bankada kan kudin fansho

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewar ta biya tsohon...

Gwamnatin Kano ta bada hutun sabuwar shekarar Musulunci

Gwamnatin Jihar Kano ta ayyana ranar Talata, 16 ga...

2027: Dan Kwankwaso ya zama dan takarar mataimakin gwamnan Kano a NDC

Dan takarar gwamnan Jihar Kano na jam'iyyar NDC a...

Yadda Tallafin Sanata Barau na N100,000 Ke Sauya Rayuwar ‘Yan Kasuwa da Manoma a Kano ta Arewa

Malama Habiba, mai soyar da gyada a garin Gwarzo...