Shugaban Ƙungiyar Ma’aikatan Rediyo, Talabijin, Wasan Kwaikwayo, Fasaha da Al’adu (RATTAWU) reshen Jihar Kano, Kwamared Babangida Mahmouda Biyamusu, tare da mambobin Majalisar Zartarwa ta ƙungiyar, sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayi Alhaji Adamu Ibrahim Getso, tsohon Darakta Janar na ARTV kuma tsohon Manajan Darakta na Radio Kano, wanda ya rasu bayan fama da rashin lafiya.
Ziyarar ta kasance ne domin jajanta wa iyalan mamacin tare da nuna alhini kan babban rashi da aka yi a harkar yaɗa labarai da al’ummar Jihar Kano baki ɗaya.

Da yake jawabi yayin ziyarar, Kwamared Babangida Mahmouda Biyamusu ya bayyana rasuwar Alhaji Adamu Ibrahim Getso a matsayin babban gibi ga masana’antar yaɗa labarai, yana mai cewa marigayin ya sadaukar da rayuwarsa wajen hidimtawa al’umma, wayar da kai da kuma horar da ƙwararrun ma’aikatan yaɗa labarai tsawon shekaru.
Ya ce marigayin ya kasance mutum mai ƙwarewa, nagarta da kishin aiki, wanda ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen bunƙasa gidajen rediyo da talabijin a Kano da ma ƙasa baki ɗaya.
Shugaban RATTAWU ya ƙara da cewa kyawawan halaye da ayyukan alherin da marigayin ya bari za su ci gaba da zama abin koyi ga masu tasowa a harkar aikin jarida da watsa labarai.
A madadin RATTAWU reshen Jihar Kano, Kwamared Babangida Mahmouda Biyamusu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalan mamacin, abokan aikinsa, ɗalibansa da daukacin al’ummar jihar, tare da addu’ar Allah Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya yalwata masa rahama, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa, sannan Ya bai wa iyalansa da masoyansa juriyar jure wannan babban rashi.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na Kungiyar Mustapha Idris Yola ya sanyawa hannu kuma aka aikowa Kadaura24 sun yi addu’ar Allah Ya jiƙan Alhaji Adamu Ibrahim Getso, Ya sa Aljanna ce makomarsa. Amin.