Kungiyar Ɗaliban Mariri ta gudanar da aikin duba marasa Lafiya kyauta a yankin

Date:

Daga Abdallahi Shu’aibu Hayewa

 

Kungiyar Dalibai ta Makarantar Mariri wato Mariri Student Association ta gudanar da gagarumin taron duba lafiyar al’umma kyauta tare da wayar da kan al’ummar yankin, domin karfafa musu gwiwa wajen kula da lafiyarsu don gano cututtukan dake damun mutum domin daukar matakin gaggauwa.

Da take ganawa da Jaridar Kadaura24 shugaban kungiyar Daliban ta Mariri Kwamared Aminu Danladi ya bayyana cewa manufar taron ita ce domin su tallafawa al’umma musamman masu karamin karfi da ba su da damar yin gwaje-gwajen asibiti akai-akai.

InShot 20250309 102512486

Kwamared Aminu Danladi ya ce wannan mataki wani bangare ne na ci gaba da shirye-shiryen kungiyar wajen tabbatar da cewa al’umma sun san muhimmancin kula da lafiya, da yin gwaje-gwajen duba lafiyarsu akai-akai domin kare kansu daga kamuwa da cututtuka masu tsanani.

Ya kara da cewa kungiyar za ta ci gaba da gudanar da irin wadannan shirye-shirye a lokuta daban-daban domin ciyar da al’umma gaba ta fuskar kula da lafiya da ilimi.

A nasa jawabin Dagacin Mariri Alhaji Saminu Madaki ya nuna jin dadinsa tare mika godiyarsa ga wannan kungiyar ta daliban Maririn, bisa wannan kokarin da sukayi.

Gwamnan Taraba ya bayyana dalilinsa na shirin komawa APC

” Babu shakka Wannan aikin da wannan kungiyar ta yi wa al’ummarmu abun a Yana ne, kuma Muna kira ga sauran kungiyoyi Irin wadannan da zu yi koyi da Wannan kungiya domin tallafawa al’umma masu karamin karfi”. Inji Dagacin

Wasu daga cikin wadanda su ka amfana da wannan shirin sun bayyana farin cikinsu bisa wannan aiki, tare da mika godiya ga kungiyar saboda irin gudunmawar da take bayarwa wajen tallafa wa lafiyar jama’a a yankin.

A yayin taron, an gudanar da muhimman gwaje-gwaje da suka haɗa da, Gwajin cutar Hanta, Hawan Jini da kuma Gwajin Ciwon shuga, Wanda ya samu Halartar Iyaye Maza da mata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnan Taraba ya bayyana dalilinsa na shirin komawa APC

Gwamnan jihar Taraba, Agbu Kefas, ya ce zai shiga...

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...