Shugaban Karamar Hukumar Ungogo Ya Raba Kwamfutoci Ga Daliban da Suka Samu Tallafin Karatu Zuwa Kasar Indiya

Date:

Shugaban Karamar Hukumar Ungogo, Hon. Tijjani Amiru Bilyaminu Rangaza, ya raba na’uarori masu kwakwalwa (kwamfutoci) ga dalibai goma sha biyu ‘yan asalin Ungogo da Gwamnatin Jihar Kano ta ba su tallafin karatun digiri na biyu (Master’s Degree) a kasar Indiya.

An gudanar da bikin bayar da kayan a harabar sakatariyar karamar hukumar, inda Hon. Rangaza ya shawarci daliban da su kasance jakadun Ungogo na gari tare da mayar da hankali kan karatunsu.

FB IMG 1753738820016
Talla

Ya jaddada cewa ilimi shi ne ginshikin ci gaban kowace al’umma, don haka karamar hukumar ta yanke shawarar tallafa musu da kwamfutoci domin sauƙaƙa musu karatu da kuma karfafar su wajen amfani da sabbin hanyoyin karatu na zamani.

Shugaban ya yi musu fatan alheri, tare da addu’ar Allah ya basu nasara da dawowa lafiya.

Shugaba Tinubu ya nemi Majalisar Dattawa ta tabbatar da sabbin hafsoshin tsaro

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na yankin Usman Muhammad Kabir ya sanyawa hannu , ya ce Wasu daga cikin daliban da suka amfana, Jibrin Musa Uba da Kabiru Auwal Sale, sun bayyana farin cikinsu tare da godewa shugaban bisa wannan kyauta, suna mai alkawarin yin amfani da kwamfutocin yadda ya kamata wajen karatun su.

Bikin ya gudana a sakatariyar Karamar Hukumar Ungogo, inda manyan baki da suka halarta suka haɗa da shugabannin siyasa, kansiloli, iyaye da sauran jama’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Cire Maryam Sanda Daga Jerin Wadanda Za a Yi Wa Afuwa

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya bada umarnin a...

Majalisar Kano ta buƙaci a soke ɗaukar aikin kwastam da aka yi a kwanan nan

Majalisar dokokin jihar Kano ta yi kira ga dukkan...

‎ ‎Kuskure ne Tinubu ya cigaba da ciyo wa Nigeria bashi bayan ya cire tallafin mai – Sarki Sanusi

‎ ‎ ‎Sarkin Kano kuma tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN),...

Shugaba Tinubu ya nemi Majalisar Dattawa ta tabbatar da sabbin hafsoshin tsaro

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aika wa Majalisar...