Kashim Shattima ya sauka daga kujerar ta mataimakin shugaban Nigeria ya baiwa wata yarinya

Date:

Mataimakin shugaban Kasa Kashim Shattima ya sauka daga kujerarsa ,inda ya baiwa wata yarinya ta hau kujerar na wucin gadi.

A jiya, a fadar shugaban ƙasa, mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya gana da tawagar PLAN International ƙarƙashin jagorancin Helen Mfonobong Idiong, daraktar shirye-shirye da kirkire-kirkire ta ƙungiyar.

A yayin ziyarar, Shettima ya bai wa wata yarinya mai suna Joy Ogah damar zama mataimakin shugaban ƙasa na wucin gadi, inda ta yi jawabi ga al’umma.

Yayin da yake jawabi a wajen taron, Mataimakin Shugaban Ƙasa ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki da sauran al’umma cewa, Shugaba Bola Ahmad Tinubu na da cikakken ƙuduri wajen inganta ilimin ’ya’ya mata a fadin Najeriya.

RMK@69: Tinubu ya yi wa Kwankwaso kyakykyawan yabo

Ya ce, daga cikin manufofin gwamnati na tallafa wa ilimin ’ya’ya mata, shirin ciyar da ɗalibai a makarantu na daga cikin muhimman matakai da ake aiwatarwa.

Haka kuma, ya bayyana Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, a matsayin wacce ya kamata a rika koyi da ita , saboda yadda take taimakom ya’ya mata domin su zamo masu dogaro da kanwunansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...

RMK@69: Kwankwaso Jagora Ne Mai Hangen Nesa, Abba Kuma Na Kawo Ci Gaba a Kano – Bakwana

Wani jigo a kungiyar Kwankwasiyya, kuma tsohon mai ba...

Da dumi-dumi: Tinubu ya nada sabon Minista

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya aike da sunan...

Gwamnatin Kano ta baiyana lokacin da za ta kammala aikin gadojin sama na Tal’udu da Dan’Agundi — Kwamishina

Gwamnatin Jihar Kano ta sake jaddada aniyarta na kammala...