Dalilin Kano Pillars na dakatar da mai horaswarta

Date:

Shugabancin ƙungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ya sanar da dakatar da Mai horas da ƴan wasa na ƙungiyar, Ogenyi Evans, da Babban Kocin ta, Ahmed Garba (Yaro Yaro), nan take, sakamakon rashin gamsasshen sakamakon da ƙungiyar ke samu a kakar gasar Firemiya ta ƙasa .

Wannan na ƙunshe ne cikin sanarwar da Sashen Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na ƙungiyar ya fitar a jiya Lahadi, inda shugabancin kungiyar ya bayyana damuwarta kan yadda ƙungiyar ke samun sakamako maras kyau.

Pillars ta buga wasanni 8 zuwa yanzu, inda ta samu nasara a wasanni 2 kacal, ta yi kunnen doki 2 sannan ta sha kashi a wasanni 4.

“Wannan mataki ya zama dole sakamakon yadda ƙungiyar ke yin wasanni marasa kyau wanda bai dace da tsammanin hukumar gudanarwa da magoya bayan ƙungiyar ba,” in ji sanarwar.

A halin yanzu, tsohon kyaftin ɗin ƙungiyar kuma Mataimakin Koci, Gambo Muhammad, zai jagoranci harkokin horo na ƙungiyar na ɗan lokaci. Zai yi aiki tare da Kocin masu tsaron gida, Suleiman Shuaibu.

Ƙungiyar Kano Pillars, wadda aka fi sani da Sai Masu Gida, na fatan wannan sauyi zai taimaka wajen farfaɗo da ƙungiyar a ci gaba da kakar gasar NPFL.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...

RMK@69: Kwankwaso Jagora Ne Mai Hangen Nesa, Abba Kuma Na Kawo Ci Gaba a Kano – Bakwana

Wani jigo a kungiyar Kwankwasiyya, kuma tsohon mai ba...

Da dumi-dumi: Tinubu ya nada sabon Minista

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya aike da sunan...

Kashim Shattima ya sauka daga kujerar ta mataimakin shugaban Nigeria ya baiwa wata yarinya

Mataimakin shugaban Kasa Kashim Shattima ya sauka daga kujerarsa...