Yan Uwa da Abokan Arzikin Sabon Kwamishinan Shari’a na Kano Sun Shirya masa addu’o’i na musamman

Date:

Yan uwa da abokan arziki na kwamishinan shari’a na jihar Kano Abdulkarim Maude SAN sun shirya masa saukar Alqur’ani mai girma da kuma addu’o’i na musamman domin ya sami nasarar fara aikin da gwamnan Kano ya dora masa .

Alarammomi da dama ne suka hadu da yan uwan sabon kwamishinan domin gudanar da addu’o’in a Unguwar Kwana hudu dake karamar hukumar Nasarawa inda Abdulkarim Maude ya tashi.

Da yake zanyawa da wakilin Kadaura24 bayan kammala sauka da addu’in Guda cikin makusantan sabon Kwamishinan mai suna Usman Abdu ya ce sun shirya taron addu’o’in ne domin nemawa Abdulkarim Maude SAN taimakon Allah a aikin da gwamnan Kano ya ba shi.

” Nan da ka ke gani yan uwa ne da abokan arziki da su ka tashi tare da sabon Kwamishinan Shari’a su ka hadu domin yi masa addu’o’i na musamman bayan saukar Alqur’ani mai girma don nema masa Allah ya Bashir nasarar sauke nauyin da gwamnan ya dora masa”. A cewar Usman Abdu

Ya ce dama kwamishinan ya saba shirya Irin wadannan addu’o’i ga Gwamnan Kano musamman lokacin da ake shari’a da kuma lokacin da yake yakin neman zabe, haka ta sa muma yanzu muka shirya masa don ganin ya sami taimakon Allah Madaukakin Sarki .

” Muna da kwarin gwiwar Abdulkarim Maude zai yi aiki tsani da Allah kuma zai yi abun da bama a tsammani daga gare shi, saboda kwararren lauya ne kuma mutum ne mai taimakon mutane , don haka muka baiwa gwamnan Kano tabbacin Abdulkarim ba zai ba shi kunya ba”. Inji Usman Abdu

Usman Abdu ya ce sun alkawarin cigaba da shiryawa Kwamishinan shari’a na jihar Kano Irin wadannan addu’o’i na musamman domin ya sami nasarar a aikin da gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya dora masa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Tinubu ya ba da Umarnin rage kudin aikin Hajjin 2026

Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya umarci hukumar kula...

Hukumar yaƙi da cin-hanci ta jihar Kano ta fara binciken Ganduje kan zargin karkatar da Naira biliyan 4 a Kano

Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci da...

Ƙungiyar Forum of Progressive Academics ta Yi Allah-wadai da Yunkurin Siyasantar da Bikin Cikar Najeriya Shekara 65 a Kano

Ƙungiyar Forum of Progressive Academics (FPA) ta yi Allah-wadai...

Sanata Barau zai raba Naira 20,000 ga mutane 10,000 a Jihar Kano

Mataimakin shugaban majalaisar dattawan Nigeria Sanata Barau Jibrin zai...