Nigeria@65:Gwamnatin tarayya ta soke fareti na ranar yancin kai

Date:

 

Gwamnatin Tarayya ta sanar da soke bikin fareti na ranar tunawa da samun ’yancin kai wanda aka shirya gudanarwa a ranar Laraba, 1 ga Oktoba, 2025, domin cika shekaru 65 da samun ’yancin kai.

Wata sanarwa da Daraktan Sashen yada labarai na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Segun Imohiosen, ya fitar ta bayyana cewa soke bikin fareti bai rage muhimmancin wannan babban tarihi ba, domin gwamnati ta jajirce wajen murnar cika shekaru 65 da samun ’yancin kai da mutunci da kuma kwazo.

Sanarwar ta ƙara da cewa, duk sauran shirye-shiryen da aka tanada domin bikin ranar ’yancin kai za su gudana kamar yadda aka tsara.

Haka kuma, gwamnati ta yaba da fahimta, goyon baya da haɗin kan ’yan Najeriya baki ɗaya, mambobin ƙungiyoyin diflomasiyya da kuma baƙi na musamman. Ta kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su ci gaba da mara wa gyare-gyaren Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya domin gina ƙasa mai ɗaukaka, in ji sanarwar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Tinubu ya ba da Umarnin rage kudin aikin Hajjin 2026

Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya umarci hukumar kula...

Hukumar yaƙi da cin-hanci ta jihar Kano ta fara binciken Ganduje kan zargin karkatar da Naira biliyan 4 a Kano

Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci da...

Ƙungiyar Forum of Progressive Academics ta Yi Allah-wadai da Yunkurin Siyasantar da Bikin Cikar Najeriya Shekara 65 a Kano

Ƙungiyar Forum of Progressive Academics (FPA) ta yi Allah-wadai...

Yan Uwa da Abokan Arzikin Sabon Kwamishinan Shari’a na Kano Sun Shirya masa addu’o’i na musamman

Yan uwa da abokan arziki na kwamishinan shari'a na...