Nigeria@65:Gwamnatin tarayya ta soke fareti na ranar yancin kai

Date:

 

Gwamnatin Tarayya ta sanar da soke bikin fareti na ranar tunawa da samun ’yancin kai wanda aka shirya gudanarwa a ranar Laraba, 1 ga Oktoba, 2025, domin cika shekaru 65 da samun ’yancin kai.

Wata sanarwa da Daraktan Sashen yada labarai na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Segun Imohiosen, ya fitar ta bayyana cewa soke bikin fareti bai rage muhimmancin wannan babban tarihi ba, domin gwamnati ta jajirce wajen murnar cika shekaru 65 da samun ’yancin kai da mutunci da kuma kwazo.

Sanarwar ta ƙara da cewa, duk sauran shirye-shiryen da aka tanada domin bikin ranar ’yancin kai za su gudana kamar yadda aka tsara.

Haka kuma, gwamnati ta yaba da fahimta, goyon baya da haɗin kan ’yan Najeriya baki ɗaya, mambobin ƙungiyoyin diflomasiyya da kuma baƙi na musamman. Ta kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su ci gaba da mara wa gyare-gyaren Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya domin gina ƙasa mai ɗaukaka, in ji sanarwar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...