Ziyarar Aiki: Shugaba Tinubu Ya Iso Lagos

Date:

Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya isa birnin Lagos a ranar Juma’a domin ziyarar aiki , yayin da Najeriya ke shirin bikin cikar ta shekaru 65 da samun ‘yancin kai a cikin salo na takaita bikin

Shugaban Ƙasan ya je Lagos ne bayan halartar bikin nadin Sarkin Ibadan, Oba Rashidi Ladoja, a tsohon birnin Ibadan dake jihar Oyo.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Kasar Bayo Onanuga ya fitar .

Yace a yayin zamansa a Lagos, Shugaba Tinubu zai gana da manyan ‘yan kasuwa na ƙasar da kuma jami’an gwamnati na matakin koli.

Kazalika, a ranar Talata 30 ga Satumba, Shugaban Ƙasan zai ziyarci jihar Imo domin kaddamar da wasu muhimman ayyuka da Gwamna Hope Uzodimma ya aiwatar.

A cikin shagulgulan bikin ‘yancin kai, Shugaba Tinubu zai kuma kaddamar da sabuwar cibiyar al’adu da fasaha wadda aka chanza mata suna zuwa Cibiyar Wole Soyinka ta Al’adu da Fasaha.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar jin daɗin alhazai ta Kano ta sanar da kuɗin aikin hajjin badi

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta amince...

Kudade: Ganduje ya caccaki Gwamnatin kano

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma Tsohon shugaban jam’iyyar APC...

Gwamnan Kano ya tura sunayen mutane biyu majalisar dokokin don nada su a mukaman Kwamishinoni

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya mika...

NLC Reshen Kebbi Ta Soki Cire Naira Miliyan 14 Daga Albashin Malamai

Kungiyar Kwadago ta Ƙasa (NLC) reshen Jihar Kebbi, ta...