Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da sauyawa wasu kwamishinoni ma’aikatu, sannan kuma an sauyawa wasu ma’aikatan gwamnati a wasu muhimman ma’aikatun jihar.
Wannan na kunshe ne a cikin sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin-Tofa, ya aikowa Kadaura24.
Ya ce matakin yana daga cikin kokarin gwamnati na kara karfafa shugabanci da inganta ayyukan gwamnati a fannoni daban-daban.
A cewar sanarwar, Kwamishinan Shari’a na jihar, Barista Haruna Isa Dederi, an mayar da shi zuwa Ma’aikatar Sufuri. Haka kuma, Darakta a Ma’aikatar Shari’a, Barista Mustapha Nuruddeen Muhammad, an mayar da shi Ma’aikatar Muhalli a matsayin Babban Sakatare.

Kwamishinan Harkokin Jin Kai, wanda ya kasance mai rikon kwarya a Ma’aikatar Sufuri, zai koma ma’aikatarsa ta asali, wato ta Harkokin Jin Kai.
Gwamna Yusuf ya umurci dukkan jami’an da sauye-sauyen suka shafa da su mika ragamar ofisoshinsu ga manyan jami’an da ke cikin ma’aikatun kafin kammala aiki gobe Talata, 23 ga Satumba, 2025.
Ganduje bai bar min ko sisi a baitul malin Kano ba sai bashi –Gwamna Abba
Gwamnan ya jaddada kudirin gwamnatinsa na gaskiya, inganci da shugabanci nagari, tare da bukatar jami’an gwamnati su ba da hadin kai ga sabbin kwamishinonin domin gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.