Tinubu y ba da umarnin sake Karya farashin kayan Abinci a Nigeria

Date:

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bai wa wani kwamiti na majalisar zartarwar ta tarayya umarnin daukar karin matakai don rage farashin kayan abinci a fadin kasar nan.

Minista a Ma’aikatar Noma, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi, ne ya bayyana haka a Abuja ranar Laraba.

Sanata Abdullahi ya bayyana cewa za a aiwatar da wannan umarni ta hanyar tabbatar da tsaro domin wucewa da kayayyakin amfanin gona da sauran kayan abinci cikin kwanciyar hankali a kan manyan hanyoyi a duk fadin Najeriya.

Hasashe 6 da Musa Iliyasu Kwankwaso ya yi kuma suka tabbata a siyasar Kano

Ya kara da cewa wannan mataki na daga cikin hangen nesa na shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu wajen cimma manufar sauko da kayan abinci mai dorewa a kasar.

FB IMG 1753738820016
Talla

Ministan ya jaddada cewa kwamiti na majalisar zartarwa na ci gaba da aiki kan hanyoyin tabbatar da tsaron kayayyakin noma da saukaka jigilar su daga wuraren da ake samarwa zuwa kasuwanni a dukkan jihohin kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yin rijistar katin Zabe zata taimaki addinin musulunci da musulmai – Mal Usman Mai Dubun Isa

Shahararren mai yabon Manzon Allah (S A W) Malam...

Jami’ar MAAUN Da Kwalejin Seneca ta Canada Sun Kulla Alaka Don Inganta Kwarewar Turanci da Samar da Damar Karatu Ga Dalibai A Duniya

  Gamayyar rukunin jami’o’in MAAUN ta kulla yarjejeniyar hadin gwiwar...

Hasashe 6 da Musa Iliyasu Kwankwaso ya yi kuma suka tabbata a siyasar Kano

‎ ‎ ‎ ‎Musa Iliyasu Kwankwaso na daga cikin fitattun ’yan siyasar...

Hukumar Hisbah Za ta Tura Sama da Jami’ai 1,000 Don Samar da Tsaro a Ranar Takutaha a Kano

Hukumar Hisbah ta Karamar Hukumar Birni a Jihar Kano...