Hukumar Hisbah Za ta Tura Sama da Jami’ai 1,000 Don Samar da Tsaro a Ranar Takutaha a Kano

Date:

Hukumar Hisbah ta Karamar Hukumar Birni a Jihar Kano ta tura jami’anta sama da 1,000 domin tabbatar da tsaro a yayin bikin Takutaha, tare da fatattakar batagari da ke fakewa da bikin wajen aikata ayyukan da suka saba wa addini da al’ada.

FB IMG 1753738820016
Talla

Kwamandan Hisbah na Karamar Hukumar Birni, Ustaz Hamidan Tanko Alasaka, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya aikowa Kadaura24 a Kano.

Ya ce jami’an da aka tura sun haɗa da na musamman da za su kula da tsaro, tsafta, da kuma bin ka’idojin bikin, tare da tabbatar da cewa ba a kawo cikas ba a yayin gudanar da shagulgulan.

Ustaz Alasaka ya ƙara da cewa, a baya ana samun wasu matasa da ke amfani da wannan rana wajen aikata abubuwan da suka sabawa koyarwar addinin Musulunci, lamarin da ya haifar da matsaloli.

“Saboda haka ne muka ɗauki ƙwararan matakai domin tabbatar da cewa an gudanar da bikin cikin tsaro, natsuwa da kuma mutunta dokokin addini,” in ji kwamandan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hasashe 6 da Musa Iliyasu Kwankwaso ya yi kuma suka tabbata a siyasar Kano

‎ ‎ ‎ ‎Musa Iliyasu Kwankwaso na daga cikin fitattun ’yan siyasar...

Kotun tafi-da-gidanka ta KAROTA ta ayyana neman wani direba ruwa a jallo

Alkalin Kotun Majistare da ke gudanar da shari’ar masu...

Muna rokon gwamnatin Kano ta haramta daukar fasinjoji a bakin titi – Kungiyar Direbobin Haya

Ƙungiyar Direbobin Motocin Haya ta ƙasa reshen Kano dake...

Rijistar Zabe: Gidan Rediyon Kano Ya Ƙara Zage Dantse Wajen Wayar da Kai Kan Al’umma

Hukumar gudanarwar Gidan Rediyon jihar Kano ta ƙara kaimi...