Yanzu-yanzu: Gwamnan Kano Ya Kaddamar da Majalisar Shurah

Date:

Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da Majalisar Shurah wacce za ta riƙa bayar da shawarwari domin inganta tafiyar da mulki tare da samar da ci gaba mai ɗorewa ga al’umma.

An gudanar da bikin kaddamarwar ne a gidan gwamnatin Kano, inda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa kafa wannan majalisa na daga cikin dabarun gwamnatinsa na tabbatar da shugabanci na gaskiya, adalci da kuma shigar da jama’a cikin tafiyar da mulki.

FB IMG 1753738820016
Talla

A cewar gwamnan, Majalisar za ta mayar da hankali wajen bayar da shawarwari a muhimman fannoni kamar tattalin arziki, ilimi, lafiya, tsaro da walwalar al’umma. Ya ce gwamnatin Kano na da burin ƙarfafa hanyoyin da za su bai wa jama’a damar tofa albarkacin bakinsu domin ci gaban kowa da kowa.

Tun da farko, Sakataren Majalisar Shurah, Alhaji Shehu Wada Sagagi, ya sanar da nadin Wazirin Kano, Sheikh Sa’ad Shehu Gidado, a matsayin Shugaban majalisar, tare da Farfesa Sani Zaharaddeen a matsayin mataimaki, sannan sauran mambobi 67 da suka haɗa da malamai, ’yan kasuwa, kwararru da wakilan al’umma daga kowane yanki na jihar.

Kadaura24 ta rawaito cewa kafa wannan majalisa zai taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya, ci gaban al’umma da kuma shugabanci na gaskiya da rikon amana a jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...