NLC ta buƙaci Tinubu da ya ƙara mafi ƙarancin albashi, ta ce N70,000 ya yi kaɗan

Date:

Kungiyar Kwadago ta Ƙasa (NLC) tare da ma’aikatan gwamnatin tarayya sun bukaci gwamnati ta gaggauta sake duba mafi ƙarancin albashi na ƙasa, suna mai cewa naira 70,000 da ake biya a yanzu ya gaza ɗaukar nauyin ma’aikata.

Sakataren riko na NLC, Benson Upah, ya bayyana cewa hauhawar farashin kayayyaki da tsadar sufuri, haya da wutar lantarki sun sa kimar N70,000 ta ragu sosai, inda ma’aikata ke shiga cikin ƙuncin rayuwa.

Ya ce idan gwamnati ba ta ɗauki mataki ba, matsalar za ta tsananta.

Haka zalika, shugaban Ƙungiyar Manyan Ma’aikatan Gwamnati (ASCSN), Shehu Mohammed, ya ce tun farko ƙungiyarsu ta nemi a ɗora mafi ƙarancin albashi kan N250,000, domin N70,000 ba zai iya biyan bukatun ma’aikaci da iyalinsa ba.

Yadda Abdulmumin Kofa ya so ya yi dillancin yan Kwankwasiyya a wajen Tinubu – Hadimin Gwamnan kano

Rahotanni sun nuna cewa wasu jihohi sun riga sun ɗaga mafi ƙarancin albashi sama da na ƙasa. A Imo, Gwamna Hope Uzodinma ya amince da N104,000, yayin da Legas da Rivers suka sa N85,000, Bayelsa, Niger, Enugu da Akwa Ibom suka amince da N80,000. Jihohi irin su Ogun, Delta, Benue, Osun da Ondo suma sun ɗaga albashin fiye da N70,000.

 

Wasu ma’aikatan gwamnati da suka yi magana da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) sun koka da tsadar rayuwa, suna mai cewa kuɗin da suke samu ba ya isa biyan haya, kuɗin makaranta da abinci. Sun bukaci gwamnatin tarayya ta ɗaga albashi zuwa akalla N150,000 domin farfaɗo da tattalin arziki da kuma inganta jin daɗin ma’aikata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...