Ku rika amfani da Sabon tsarin koyarwa da gwamnatin Kano take daukar nauyin koya muku – Sakataren Ilimin Kiru ga Malaman Firamare

Date:

Daga Shehu Hussaini Getso

Sakataren Ilimi na Karamar Hukumar Kiru, Alhaji Ayuba Garba Gajale, ya bukaci malaman makarantu na fannin kimiyya da ke cikin kananan hukumomin Kiru, Bebeji, Tudun Wada, Doguwa, Madobi, Garun Mallam, Karaye da Rogo, da su yi cikakken amfani da sabon tsarin horaswa da Gwamnatin Kano ta samar domin inganta harkokin koyarwa a yankunansu

Alhaji Gajale ya yi wannan kira ne a karshen makon da ya gabata, yayin rufe taron horaswas da aka shirya wa wasu daga cikin malamai a Kafin Miyaki Model Primary School, da ke cikin Karamar Hukumar Kiru.

Ya bayyana cewa aikin koyarwa muhimmin aiki ne da ke da nasaba kai tsaye da ci gaban kowace al’umma, don haka ya bukaci mahalarta taron da su yi amfani da abin da suka koya wajen ilmantar da dalibansu cikin yanayin da ya dace da zamani.

A cewar sa, Gwamnatin Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf na baiwa fannin ilimi kulawa ta musamman, musamman wajen samar da kayan koyo da koyarwa, gina sababbin makarantu, da kuma inganta walwalar malamai ta fuskar albashi da karin girma a duk lokacin da ya dace.

A karshe, Sakataren ya yabawa Shugaban Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Kano (SUBEB), Alhaji Yusuf Kabir Gaya, bisa cikakken hadin kai da goyon baya da yake bai wa fannin a koda yaushe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...