Kungiyar Masu amfani da Ruwan Hadeje-Jama’are ta Zaɓi Sabon Shugaba

Date:

Daga Safyan Dantala Jobawa

Kungiyar masu amfani da ruwan Haɗejiya da Jama’are (WUA) ta amince da sakatarenta, Alhaji Mustapha Adamu Mudawa, a matsayin sabon shugabanta.

Wannan ya biyo bayan ƙarewar wa’adin shugabancin kungiyar na baya, inda aka gudanar da taron tabbatar da sabon shugabanci a matakai daban-daban domin ƙara kawo ci gaban harkar noma a kogunan Haɗejiya da Jama’are da ke cikin ƙananan hukumomin Kura, Bunkure da Garun Malam.

Kungiyar ta bayyana cewa zaɓen Mudawa ya yi daidai da irin namijin ƙoƙarinsa wajen kare muradun manoma, don haka ta yanke shawarar damƙa masa wannan muƙami domin ƙarfafa cigaban manoman yankin.

CSOs sun yi Zanga-Zangar Adawa da Rashawa kan Zargin Satar Naira Biliyan 6.5 a Ofishin DG Protocol na Kano

Da yake jawabi, sabon shugaban, Alhaji Mustapha Adamu Mudawa, ya roƙi mambobin kungiyar da su haɗa kai wajen kare muradun manoma da inganta harkar noma kamar yadda aka san kungiyar da wannan aiki tun farko.

FB IMG 1753738820016
Talla

Haka kuma, kungiyar ta amince da naɗin Malam Sama’ila Sani Shirye a matsayin mataimakin shugaban kungiyar.

Taron ya samu halartar manoma da dama tare da wakilan shugabanci na kogunan Haɗejiya da Jama’are, inda aka gudanar da shi a ɗakin taro na Haɗejiya da Jama’are da ke karamar hukumar Kura.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...