Kwamitin Ganduje Kan Koran Jami’an Hisba A Kano Ya Fara Aiki

Date:

Kwamitin da tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya kafa domin bincikar korar jami’an Hisba da gwamnatin Kano ta yi ya fara zaman sa na farko.

Babban Darakta Janar na Hukumar Samar da Ayyuka ta Kasa, Dr. Baffa Babba Dan’Agundi, shi ne shugaban kwamitin, wanda ya ce sun fara aikin tantance jami’an Hisba da aka sallama daga aiki domin neman musu makoma.

Kwamitin, wanda ya kunshi mutum bakwai, ya amince da kafa wakilai 44 daga kowace karamar hukuma ta jihar Kano domin gudanar da bincike a matakin kasa.

Ribado ya magantu Kan zargin da El-Rufai ya yiwa Gwamnatin tarayya game da yan bindiga

Rahotanni sun ce za a yi amfani da kananan kwamitocin ne wajen tabbatar da gaskiyar korar jami’an Hisba da adadinsu ya kai kusan 1,000 da gwamnatin Kano ta sallama.

Haka kuma, babban kwamitin ya amince da kafa wani kwamiti na mutum uku da zai tabbatar da tsayar da mutum daya daga kowace karamar hukuma domin wakilci a gaba.

FB IMG 1753738820016
Talla

A cewar shugabannin kwamitin, za a sake gudanar da wani zama a karshen mako domin karbar rahoton da kananan kwamitoci za su gabatar kafin daukar matakin gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...