Zan tsaya takarar shugaban ƙasar Nigeria a 2027 – Atiku Abubakar

Date:

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya tabbatar da aniyarsa ta sake tsayawa takarar shugaban ƙasa a 2027, inda ya ce dole ne a ceto Najeriya daga halin matsanancin talauci da rashin adalci da ake ciki.

Atiku ya nesanta kansa daga kalaman Farfesa Ola Olateju, wanda ya ce ba ya da niyyar zama shugaban ƙasa a kowace hanya, inda ya jaddada cewa shi kansa zai tsaya takara don jagorantar farfaɗo da ƙasar.

Ya ce haɗin gwiwar jam’iyyar ADC, da shi ma memba ne, za ta kawo babban sauyi a zaben 2027.

FB IMG 1753738820016
Talla

Atiku, wanda yanzu yana da shekara 78, ya riga ya tsaya takarar shugaban ƙasa sau uku a baya (2007, 2019 da 2023), kuma zai kasance yana da shekara 81 a lokacin zaben 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...