Zan tsaya takarar shugaban ƙasar Nigeria a 2027 – Atiku Abubakar

Date:

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya tabbatar da aniyarsa ta sake tsayawa takarar shugaban ƙasa a 2027, inda ya ce dole ne a ceto Najeriya daga halin matsanancin talauci da rashin adalci da ake ciki.

Atiku ya nesanta kansa daga kalaman Farfesa Ola Olateju, wanda ya ce ba ya da niyyar zama shugaban ƙasa a kowace hanya, inda ya jaddada cewa shi kansa zai tsaya takara don jagorantar farfaɗo da ƙasar.

Ya ce haɗin gwiwar jam’iyyar ADC, da shi ma memba ne, za ta kawo babban sauyi a zaben 2027.

FB IMG 1753738820016
Talla

Atiku, wanda yanzu yana da shekara 78, ya riga ya tsaya takarar shugaban ƙasa sau uku a baya (2007, 2019 da 2023), kuma zai kasance yana da shekara 81 a lokacin zaben 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...