Magoya bayan Barr Ibrahim Isa (Matawallen Gwagwarwa) sun aikawa Gwamnan Kano Budaddiyar Wasika

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

Kira don nemawa Barr. Ibrahim Isa Aliyu (Matawallen Gwagwarwa) makoma a gwamnatinka

Ya Mai Girma Gwamna Abba Kabir Yusuf

Na rubuta wannan wasiƙar a matsayina na ɗan ƙasa kuma Wanda yake ba da gudunmawa wajen ci gaban dimokuradiyyar jiharmu ta Kano.

FB IMG 1753738820016
Talla

A tsawon lokacin da ka dauka kana fafutukar neman gwamnan Kano har ka yi nasarar shiga ofis, daidaikun mutane da dama sun tsaya tsayin daka a wajenka ganin ka Sami wannan nasarar kuma daga wadancan yan kishin Kasar a cikinsu har da BARR. Ibrahim Isah Aliyu, wanda aka fi sani da MATAWALLEN GWAGWARWA.

Wannan matashin ya bayar da gudunmawa da karfinsa, basirarsa, da dukiyarsa wajen yakin neman zabe kuma bai yi haka don amfanin kansa ba, sai don Samar da shugabanci na gari a jiharmu. Ya tattara goyon baya, don ganin sun zabe ka sun kuma Kare kuri’un da yin duk abun da ya kamata .

Bukatun Nigeria da Tinubu ya mika a taron da ake yi a Japan

Amma duk da Wannan kokarin da Barr. Ibrahim Isa ya yi har yanzu ba wani abu da aka yi masa da yake nuna yabawa bisa kokarin da yayi don kafuwar Wannan gwamnati. Rashin ba shi dama a wannan gwamnatin ya jefa matasa da dama cikin damuwa .

Ba mu rubuta wannan wasiƙar don neman gwamnan Kano ya yabawa wadanda suka ba shi gudunmawa, Muna tunasar da gwamnan cewa Idan aka yi watsi da masoya irin su Matawallen Gwagwarwa, hakan yana Sagar da gwiwar masoya . Amma idan aka karrama su aka yabawa musu hakan yana kara dankon soyayya tsakanin gwamnati da wadanda ake mulka.

Don haka muna kira ga gwamnatin Abba Kabir Yusuf da ta duba gudunmawar da Barr. Ibrahim Isa Aliyu da makamantansa su ka bayar. Tabbas yin hakan zai karawa magoya bayan kwarin gwaiwar cigaba da ba da gudunmawa.

Tare da matuƙar girmamawa,

Comr. Nasir Danjuma Gwagwarwa

Daga kungiyar Muryar al’umma tun daga Tushen Tushen

Jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...