Kwankwaso ya yi tsokaci game da zaben cike gurbi da akai a Kano

Date:

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana godiya ga mutanen mazabar Bagwai da Shanono bisa goyon bayan da suka nuna wa jam’iyyar a zaɓen cike gurbi da aka kammala.

A wata sanarwa da ya fitar a yau Lahadi, Kwankwaso ya bayyana nasarar ɗan takarar NNPP, Ali Lawan Alhassan, a matsayin babbar nasara, ya na mai cewa hakan ya nuna a fili inda amincin jama’a ya ke yanzu da nan gaba.

FB IMG 1753738820016
Talla

Ya kuma yabawa shugabanni da magoya bayan jam’iyyar bisa jajircewa da kuma gudanar da zaɓen cikin lumana da tsari na dimokuraɗiyya.

A Hukuma ce INEC ta bayyana sakamakon zabukan cike gurbi da aka yi a kano

“Mutanen Bagwai da Shanono sun yi magana a bayyane ta hanyar kada ƙuri’a mai tarin yawa ga jam’iyyar NNPP. Nasarar da Ali Lawan Alhassan ya samu a fili take cewa ga inda amincin jama’armu yake, yanzu da nan gaba,” in ji Kwankwaso.

Ya ƙara jinjinawa jajircewar ‘yan jam’iyyar da magoya baya da suka yi aiki tukuru domin tabbatar da gudanar da zaɓen cike gurbin cikin lumana da nasara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Tinubu ya ba da Umarnin rage kudin aikin Hajjin 2026

Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya umarci hukumar kula...

Hukumar yaƙi da cin-hanci ta jihar Kano ta fara binciken Ganduje kan zargin karkatar da Naira biliyan 4 a Kano

Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci da...

Ƙungiyar Forum of Progressive Academics ta Yi Allah-wadai da Yunkurin Siyasantar da Bikin Cikar Najeriya Shekara 65 a Kano

Ƙungiyar Forum of Progressive Academics (FPA) ta yi Allah-wadai...

Yan Uwa da Abokan Arzikin Sabon Kwamishinan Shari’a na Kano Sun Shirya masa addu’o’i na musamman

Yan uwa da abokan arziki na kwamishinan shari'a na...