Gwamnatin Kano ta sanar da Ranar Fara hutun zangon Karatu na 3 ga ɗaliban jihar

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da ranar Juma’a 25 ga Yuli, 2025 a matsayin ranar da za a fara hutun zangon Karatu na 3 ga dukkan daliban makarantun kwana da makarantun firamare masu zaman kansu da na gaba da sakandare a jihar.

Don haka ana buƙatar iyayen da su je Makarantun ya’yansu don dauko ya’yansu da sanyin safiyar Juma’a 25 ga Yuli, 2025.

InShot 20250309 102512486
Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi ta jihar Balarabe Abdullahi Kiru ya fitar .

Sanarwar ta bayyana cewa daliban makarantun kwana za su koma Makaranta a ranar Lahadi 7 ga watan Satumba 2025, yayin da daliban makarantun jekaka- dawo za su koma ranar Litinin 8 ga Satumba, 2025.

Gwamnatin Kano za ta fara jiyo ra’ayoyin al’umma kafin gudanar da duk wani aiki a jihar – Bilkisu Indabo

Kadaura24 ta ruwaito Kwamishinan Ma’aikatar Dakta Ali Haruna Makoda ya yi kira ga Iyaye da Dalibai da su tabbatar sun bin ka’idojin da aka amince da su na komawa Makarantun ya’yansu.

Dakta Makoda ya yi gargadin cewa za a dauki matakin ladabtarwa a kan daliban da suka karya dokokin komawa Makaranta.

Ya kuma godewa Iyayen yara bisa Hadin Kai da goyon baya da suke baiwa gwamnatin jihar Kano .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar cigaban Ilimi da gyaran tarbiya ta unguwar zango ta shirya taron kan tarbiyya da tsaro

Daga Rahama Umar Kwaru   Wani Malami a jami'ar Bayero dake...

Gwamnatin Kano za ta fara jiyo ra’ayoyin al’umma kafin gudanar da duk wani aiki a jihar – Bilkisu Indabo

Daga Samira Hassan   Gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin nan...

Kwankwaso ya gana da Tinubu a fadar shugaban kasa

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso,...

Neman Ilimin addini dana boko da sana’a ba kishiyoyin juna ba ne – Dr. Aminu Sagagi ga matasan Zango

Daga Rahama Umar Kwaru   Wani Malamin addinin musulunci a kano...