Gwamnatin Jihar Kano ta fara bincike kan mutuwar wasu ɗaliban makarantar Sakandare biyu

Date:

 

Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Dr. Ali Makoda, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan mutuwar ɗalibai biyu a makarantar Kwana Sakandare da ke Bichi.

Ɗaliban da suka rasu, Hamza Tofawa da Umar Dungurawa, ana zargin wasu abokan karatunsu ne suka kai musu hari da wani ƙarfe da ake kira “Gwale-Gwale”.

InShot 20250309 102512486
Talla

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktan Wayar da Kai na Ma’aikatar Ilimi, Balarabe Kiru, ya fitar, inda aka rabawa manema labarai ciki har da jaridar The PUNCH a ranar Laraba.

A cewar sanarwar, kwamishinan, ta bakin Babban Sakataren Ma’aikatar, Bashir Muhammad, ya tabbatar wa jama’a cewa gwamnatin jihar za ta gudanar da bincike mai adalci da gaskiya tare da tabbatar da cewa kowa ya samu hakkinsa.

Kamfanin Yahuza Suya Ya aike da Sakon ta’aziyyar Rasuwar tsohon shugaban Kasa Buhari

“An bayar da rahoton cewa wannan mummunan aiki ya faru ne bayan wasu manyan ɗalibai sun yanke shawarar hukunta waɗanda suka rasu bisa zargin aikata wani laifi,” in ji shi.

Babban Sakataren, wanda ya kai ziyara makarantar, ya ja hankalin ɗalibai da su zama masu lura da kuma kaucewa ɗaukar doka a hannunsu.

“Ku guji ɗaukar doka a hannunku, ku tabbata duk wani abin da ya dame ku kun kai rahoto ga hukumomin makaranta don ɗaukar mataki da ya dace,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Atiku Abubakar ya fice daga jam’iyyar PDP

Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya fice daga...

Kamfanin Yahuza Suya Ya aike da Sakon ta’aziyyar Rasuwar tsohon shugaban Kasa Buhari

Shugaban kamfanin Yahuza Suya and Catering Services Nig. Limited,...

Yadda aka Binne Gawar Buhari a gidansa dake Daura

An binne gawar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a...

Yadda mu ka yi da Buhari kwana daya kafin rasuwarsa – Mamman Daura

    Alhaji Mamman Daura, ɗan uwan marigayi Shugaba Muhammadu Buhari,...