Kotu ba da umarnin mayar da Natasha bakin aikinta

Date:

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar Dattijai da ta dawo da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, wadda aka dakatar.

Yayin yanke hukunci, Mai Shari’a Binta Nyako ta bayyana cewa dakatar da Natasha na tsawon watanni shida ya yi tsauri fiye da kima.

InShot 20250309 102512486
Talla

Kotun ta ce Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, bai yi kuskure ba lokacin da ya hana Natasha magana a zauren majalisa, saboda a lokacin ba ta zaune kan kujerar da aka ware mata ba. Sai dai kotun ta bukaci Natasha ta bai wa majalisar hakuri.

A cewar kotun, tun da majalisa tana da kwanaki 181 a kowanne zango, dakatar da Natasha tsawon watanni shida ya yi kama da hana mazaɓarta wakilci har na kusan kwanaki 180.

Yadda Shugabanni da jagororin Jam’iyyar APC na Kano suka kauracewa tarbar Kashim Shattima yayi ziyarar ta’aziyya

Kotun ta jaddada cewa duk da cewa majalisar na da ikon ladabtar da ɗan majalisa, bai kamata hukuncin ya kai ga hana ayyukan wakilci ba.
Mai shari’a Nyako ta kuma yi watsi da ƙarar Akpabio na cewa kotun ba ta da hurumin sauraron shari’ar.

Majalisar Dattawa ta dakatar da Natasha a watan Maris bayan ta zargi Shugaban Majalisar, Sanata Godswill Akpabio, da cin zarafi ta fuskar lalata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnan Kano ya Naɗa Ahmed Musa a Matsayin Darakta Janar na Kano Pillars

Daga Zakaria Adam Jigirya   Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Yanzu:yanzu: Gwamnan kano ya yi sabbin nade-naden mukamai

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Gwamann jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Yara ɗalibai na fuskatar barazanar daina zuwa Makaranta a Hotoro saboda lalacewar hanya

Daga Isa Ahmad Getso   Al'umma da Malaman makaranta a unguwar...

Yadda Shugabanni da jagororin Jam’iyyar APC na Kano suka kauracewa tarbar Kashim Shattima yayi ziyarar ta’aziyya

Daga Fatima Mahmoud Diso   Shugabanni da jagororin jam'iyyar APC na...