Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Date:

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur daga Naira 880 zuwa N840 kowace lita.

Kakakin Rukunin kamfanoni Dangote, Anthony Chiejina, ya tabbatar wa da jaridar PUNCH cewa an rage farashin a daren ranar Litinin.

InShot 20250309 102512486
Talla

Ya ce sabon farashin ya fara aiki ne a ranar 30 ga watan Yuni.

“An rage farashin man daga N880 zuwa N840 kowace lita daga 30 ga watan Yuni,” Chiejina

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito matatar man Dangote ta kara farashin man fetur zuwa naira 880 a daidai lokacin da rikici ya barke tsakanin Isra’ila da Iran na tsawon kwanaki 12, lamarin da ya sa farashin danyen mai ya Karye akan dala 80 kan kowacce ganga.

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

A baya dai jaridar PUNCH ta ruwaito cewa ‘yan kasuwar sun yi hasashen za a iya kara farashin daga ranar Litinin.

Abokan huldar matatar Dangote irinsu MRS, Heyden da AP ana sa ran za su rage farashin na su nan ba da jimawa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...