Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin ta sakamakon rasuwar fitaccen attajiri kuma jigo a harkar kasuwanci a Najeriya, Alhaji Aminu Alhassan Dantata, wanda ya rasu yana da shekaru 94.
Rasuwar Alhaji Aminu Dantata babban rashi ne, ba ga iyalansa da al’ummarsa kawai ba, har ma ga Jihar Kano, Arewacin Najeriya da kasar baki ɗaya. Gudummawar da ya bayar a fannin kasuwanci, aikin alheri, ilimi da ci gaban addini sun bar tarihi da ba za a manta da su ba har tsawon zamani.

Alhaji Aminu Dantata mutum ne da aka girmama, jagora kuma uba ga ɗaya daga cikin manyan gidajen kasuwanci da suka fi kowa kima a Najeriya da nahiyar Afirka. Rayuwarsa ta cika da gaskiya, tawali’u da hidima ga al’umma.
Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai
A madadin mambobin kungiyar gaba ɗaya, ƙarƙashin jagorancin Comrade Shuaibu Sani Bagwai, muna jajanta wa dangin mamacin da dukkan al’ummar Najeriya bisa wannan babban rashi. Muna roƙon Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta masa, Ya jikan sa da rahama, Ya ba shi mafaka a Aljannatul Firdaus, sannan Ya bai wa iyalansa da kasa baki ɗaya haƙuri da juriyar rashin sa.
Ko da ya bar duniya, tarihi da kyakkyawar gadon da ya bari za su ci gaba da rayuwa.