Daga Rahama Umar Kwaru
Gwamnatin jihar Kano ta jaddada kudirinta na magance matsalolin karancin gidaje da suka addabi jihar .
Kwamishinan gidaje da raya birane na jihar, Arc. Ibrahim Yakubu Adamu, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da daraktocin ma’aikatar. Ya ce gwamnati na da kwarin gwiwa ga daraktocin wajen ganin ta kawo karshen kalubalen rashin gidaje a jihar.

Arc Adamu, ya bayyana cewa a cikin wata biyu da kafa ma’aikatar ta samu damar gano wuraren da ake don gina gidaje da suka hadar da Lambu a karamar hukumar Tofa, Yargaya a karamar hukumar D/Kudu da kuma kammala ayyukan gina gidaje na garuruwan Kwankwasiyya, Amana da Bandirawo, kamar yadda gwamnan Abba Kabir Yusuf yake fata.
A wata sanarwa da daraktan wayar da kan al’umma na ma’aikatar Adamu Abdullahi ya aikowa Kadaura24, ya ce Kwamishinan ya kara da cewa ma’aikatar za ta himmatu tare da bullo da wasu tsare-tsare na gidaje don bunkasa Birane da karkara.
Dr. Bashir Aliyu Umar ya Sami Babban Mukami a Nigeria
Don haka, Kwamishinan, ya shawarci Shugabannin ma’aikatar da su duk abun da ya dace don cimma burin ciyar da jihar gaba kamar yadda gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta da a gaba .
Don haka Kwamishinan ya yi kira ga Daraktocin da su sake jajircewa wajen kawo sauyi a jihar. Ya kara da cewa sabuwar ma’aikatar gidaje da raya birane ta kuduri aniyar ganin kowane dan Kano ya samu gida mai sauki da inganci.