Gwamnatin Kano ta shirya magance matsalar karancin gidaje a jihar – Kwamishinan gidaje

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Gwamnatin jihar Kano ta jaddada kudirinta na magance matsalolin karancin gidaje da suka addabi jihar .

Kwamishinan gidaje da raya birane na jihar, Arc. Ibrahim Yakubu Adamu, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da daraktocin ma’aikatar. Ya ce gwamnati na da kwarin gwiwa ga daraktocin wajen ganin ta kawo karshen kalubalen rashin gidaje a jihar.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Arc Adamu, ya bayyana cewa a cikin wata biyu da kafa ma’aikatar ta samu damar gano wuraren da ake don gina gidaje da suka hadar da Lambu a karamar hukumar Tofa, Yargaya a karamar hukumar D/Kudu da kuma kammala ayyukan gina gidaje na garuruwan Kwankwasiyya, Amana da Bandirawo, kamar yadda gwamnan Abba Kabir Yusuf yake fata.

A wata sanarwa da daraktan wayar da kan al’umma na ma’aikatar Adamu Abdullahi ya aikowa Kadaura24, ya ce Kwamishinan ya kara da cewa ma’aikatar za ta himmatu tare da bullo da wasu tsare-tsare na gidaje don bunkasa Birane da karkara.

Dr. Bashir Aliyu Umar ya Sami Babban Mukami a Nigeria

Don haka, Kwamishinan, ya shawarci Shugabannin ma’aikatar da su duk abun da ya dace don cimma burin ciyar da jihar gaba kamar yadda gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta da a gaba .

InShot 20250309 102403344

Don haka Kwamishinan ya yi kira ga Daraktocin da su sake jajircewa wajen kawo sauyi a jihar. Ya kara da cewa sabuwar ma’aikatar gidaje da raya birane ta kuduri aniyar ganin kowane dan Kano ya samu gida mai sauki da inganci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...

Ciyaman din Wudil ya kaddamar da aikin gina magudanan ruwa a wasu garuruwa a yankin

Daga Maryam Adamu Mustapha   Shugaban karamar hukumar Wudil, Hon. Abba...