Yanzu-yanzu: Ganduje ya magantu kan batun komawar Kwankwaso APC

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana jam’iyyar NNPP a matsayin wadda ba ta da sauran wani tasiri a fagen siyasar kasar, yana mai jaddada cewa jam’iyyar ta mutu, abin da ya rage kawai abinne ta.

Abdullahi Ganduje ya bayyana hakan ne yau Talata a Abuja lokacin da ya karɓi baƙuncin mambobin kungiyar goyon bayan Tinubu a wata ziyarar ban girma da su ka kai masa a sakatariyar jam’iyyar APC ta ƙasa.

IMG 20250415 WA0003
Talla

A cewar tsohon gwamnan jihar Kano, jam’iyyar NNPP tana kan kafafunta na ƙarshe kuma karshenta ya kusa.

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi ganawar sirri da Kawu Sumaila, Ali Madaki, Rurum da sauran jiga-jigan NNPP

Acewar Ganduje, ƙofar shugabancinsa a buɗe take domin yin sulhu kuma zai yi maraba da dawowar Kwankwaso cikin APC idan har ya yanke shawarar komawa jam’iyyar ta APC.

InShot 20250309 102403344

Ganduje ya kara da cewa “Shi wancan da ke kiran kansa da jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, ba mu da matsala da shi don ya ce zai dawo APC, za mu karbe shi kuma mu yi masa maraba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu ta ɗaure wani ɗan Tiktok mai wanka a tsakiyar titunan Kano

    Wata kotu a jihar Kano da ke arewacin Najeriya...

Damuna: Mun shirya inganta wuraren tsayarwar motocinmu – Kungiyoyin Direbobin na Kano

Kungiyar matuka motocin kurkura ta jihar Kano da Kungiyar...

Rasuwar Aminu Ɗantata babban rashi ne ba ga Nigeria kadai ba – Mustapha Bakwana

Daga Zakaria Adam Jigirya   Tsohon Mai baiwa gwamnan Kano shawarawa...

Gwamnatin Kano ta yabawa Tinubu saboda gyarawa da bude NCC DIGITAL PARK

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin jihar Kano ta yabawa Gwamnatin...